Labarai
Muna daf da kawo ƙarshen yajin aikin ma’aikatan shari’a- Gwamnatin Abia

Gwamnatin Jihar Abia, ta bayyana cewa ana daf da kawo ƙarshen yajin aikin da ƙungiyar ma’aikatan shari’a ta Judicial Staff Union of Nigeria ke yi, bayan samun gagarumin ci gaba a tattaunawar da ake yi tsakanin ɓangarorin biyu.
A cewar gwamnati, an samu daidaito kan muhimman batutuwa da suka haɗa da biyan alawus-alawus na hutu da kuma batun fansho, wanda ya daɗe yana ɗaya daga cikin manyan dalilan da suka haddasa yajin aikin.
Sai dai gwamnatin ta soki matsayin da kungiyar lauyoyin ta ɗauka kan lamarin, inda ta ce wasu daga cikin kalaman ƙungiyar ba su taimaka wajen warware matsalar ba, illa ma ƙara dagula al’amura.
Gwamnatin jihar ta kuma jaddada kudirinta na ci gaba da tattaunawa da JUSUN domin ganin an kawo ƙarshen yajin aikin gaba ɗaya, tare da dawo da ayyukan kotuna yadda ya kamata.
You must be logged in to post a comment Login