Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya miƙa sunan Joseph Tegbe domin nada Ministan Lantarki

Published

on

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya miƙa sunan Joseph Olasunkanmi Tegbe domin zama sabon Ministan Wutar Lantarki.

 

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Alhamis, inda ya ce an tura sunan Tegbe zuwa Majalisar Dattawa domin tantancewa da amincewa kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanada.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa, wannan naɗi na jiran sahalewar Majalisar Dattawa kafin ya zama cikakke ministan.

 

Shirin na naɗin Joseph Olasunkanmi Tegbe, dai ya biyo bayan murabus ɗin tsohon Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, wanda ya ajiye muƙaminsa domin mayar da hankali kan takarar gwamna a Jihar Oyo gabanin zaɓen shekarar 2027.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!