Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Atiku ya nemi CBN da kada su ƙara wa’adin sauya tsoffin kuɗi

Published

on

Ɗan takarar Shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar ya roƙi Babban Bankin Ƙasa CBN da kada ya ƙara wa’adin 10 ga Fabrairun da muke ciki na ci gaba da sauya tsoffin kuɗi.

Jaridar Daily Trust ta rawaito Atiku Abubakar na cewa, wasu ƴan siyasa na son amfani da damar ƙara wa’adin don yin maguɗin zaɓe.

Ya kuma roƙi CBN da ya duba yiwuwar ƙara yawan takardun sabbin kuɗin domin ragewa jama’a raɗaɗin rashin kuɗi a hannu, musamman ga mutanen da ke yankunan karkara.

Shugaban CBN dai ya sanya ranar 10 ga watan Fabrairu domin daina amfani da tsoffin kuɗi a tsakanin jama’a.

CBN ya ce, yana aiwatar da tsare-tsaren sauya fasalin kuɗi da taƙaita hada-hadar kuɗi a hannu domin sake farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasa.

LABARAI MASU ALAKA:

Wasu cikin jami’an gwamnati a fadar Villa na yi wa Tinubu zagon kasa- El-rufai

Ba a haifi Atiku a Najeriya ba, bai cancanci tsayawa takarar shugaban kasa ba – Malami

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!