Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kimiyya

Ba za mu yafewa Najeriya bashi ba – IMF

Published

on

Mambobin hukumar gudanarwar asusun bada lamuni na duniya (IMF) sun ki amincewa su sanya sunan Najeriya cikin kasashe 28 wadanda asusun na IMF zai yafe musu kudin ruwa na bashin da ya ke binsu.

 

Hukumar gudnarwar sun amince a yafe bashi ga wasu kasashe 28 wanda shine irinsa karo na uku tun bayan bullar cutar corona.

 

Da farko dai asusun na IMF ya fara daukar matakin ne a ranar 13 ga watan Afrilun 2020 kafin ya sake daukar matakin na biyu a ranar 2 ga watan Oktoba 2020.

 

Kasashe da zasu amfana da tagomashin na asusun IMF sun hada da: Afghanistan, Jamhuriyar Benin, Burkina Faso, Burundi, Jamhuriyar Afurka ta tsakiya, Chadi, Comoros, Jmahuriyar Dimukuradiyar Congo, Congo, Dibouti, Ethiopia, da kuma Gambia.

 

Sauran sune: Guinea, Guniea-BISSAU, Haiti, Liberia, Madagascar, Malawi, Mali, Mozambique, Nepal, Jamhuriyar Nijar, Rwanda, Sao Tome and Princpe, Saliyo, Solomon Island, Tajikistan, Togo da kuma Yemen.

 

A cewar shugabar asusun na IMF Kristalina Georgieva ta ce kasashen da aka yafewa sune su ka fi dandana kudarsu sakamakon cutar corona.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!