Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba mu fara sayar da takardar shiga kwalejin horas da sojoji ba – NDA

Published

on

Kwalejin horas da jami’an Soji ta Najeriya NDA ta ce har yanzu bata fara sayar da takardar shiga makarantar ba karo na saba’in da uku.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwar da jami’in hulda da jama’a na kwalejin Abubakar Abdullahi ya fitar aka kuma raba ga manema labarai.

Sanarwar ta ce rahotonnin dake yawo a kafafen sada zumunta musamman na Internet cewar, yanzu haka makarantar ta fara sayar da Form din shiga kwalejin karo na saba’in da uku ba gasakiya ba ne.

Abubakar Abdullahi ta cikin sanarwar ya kuma shawarci al’umma da su yi watsi da duk wata sanarwar dake yawo cewa kwalejin ta fara sayar da form din shiga.

Ya kuma ce makarantar za ta sanar da lokacin da za ta fara sayar da form din a duk lokacin data shirya a shafinta na Internet.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!