Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Ba za mu lamunci halasta tabar wiwi a Najeriya ba – MURIC ga majalisar wakilai

Published

on

Ƙungiyar da ke rajin kare martabar addinin islama ta Muslim Right Concern (MURIC), ta ja hankalin majalisar wakilai da cewa ka da ta kuskura ta halasta shan tabar wiwi a Najeriya.

 

Shugaban ƙungiyar farfesa Ishaq Akintola shine ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai.

 

Farfesa Akintola ya kuma soki batun haramta shan tabar wiwin yana mai cewa wasu gungun masu safarar miyagun kwayoyi ne ke son halasta tabar wiwin a Najeriya.

 

A cewar sa, a yanzu haka Najeriya tana fama da matsaloli masu yawa da suka hada da: rashin tsaro musamman rikicin boko haram da ya ki ci ya ki cinyewa ba ya ga masu satar mutane suna garkuwa da su wanda kuma kowa ya san masu aikata irin wadannan laifuka suna ta’ammali da irin wadannan miyagun kwayoyi.

 

Saboda haka farfesa Akintola ya shawarci mambobin majalisar da su yi watsi da kudirin.

 

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!