Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Babu Kasar da ke tsoma baki kan matakan da ECOWAS ke sanya wa Niger

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce babu wata kasa dake tsoma baki dangane da matakan da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Africa ta ECOWAS ke dauka kan sojojin da suka yi juyin mulki a jamhuriyar Nijar.

Ministan harkokin kasashen ketare Amb. Yusuf Maitama Tuggar ne ya bayyana hakan ta cikin wani shirin talabijin na kafar yada labarai ta dailytrust, inda ya tabo batutuwa da dama da suka shafi kungiyar ta Ecowas da jamhuriyar Nijar.

A cewar sa ‘ko a taron da kungiyar ta gudanar a baya-bayan nan a birnin tarayya Abuja, al’amuran da suka shafi jamhuriyar Nijar din ne suka kankane tattaunawar da aka gudanar a yayin taron’.

Ministan ya kara da cewa ‘na daga cikin manufofin kafa kungiyar ECOWAS, tabbatar da wanzar da zaman lafiya da cigaban tattalin arziki da kuma tabbatar da hadin kan kasashe mambobin kungiyar’.

 

Rahoton: Mukhtar Abdullahi Birnin Kudu

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!