Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Ban karbi ko sisi a hannun Magu ba – Osinbajo

Published

on

Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya musanta jita-jitar da ake yadawa cewa, ya karbi Naira Biliyan hudu daga hannun dakataccen shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC, Ibrahim Magu.

Hakan na cikin wata sanarwa ce mai dauke da sa hannun mai magana da yawun mataimakin shugaban kasa, Laolu Akande ya fitar a Abuja.
Sanarwar ta ce, ofishin mataimakin shugaban kasar ya lura da yadda wani labari ke zagaya wa a shafukan sada zumunta musamman na Twitter wadda shafukan PointBlank da Newsreel suka wallafa.

Manyan laifukan da ake zargin Ibrahim Magu

EFCC:ta sake gurfanar da Babachir Lawal tare da wasu mutane uku

EFCC na bincikar Rochas Okorocha da wasu Kusoshin Gwamnati

Ta cikin sanarwar mataimakin shugaban kasar ya bayyana labarin da cewa bashi da tushe ballantana makama.

A cewar sanarwar zargin cewa Ibrahim Magu yayi almundahanar kudaden da suka kai biliyan 39 sannan ya bashi biliyan hudu a matsayin toshiyar baki shifcin gizo ne kawai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!