Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Cutar Kwalara ta sake bulla kasar Kamaru

Published

on

A ranar Laraba gwamnatin kasar Kamaru ta bayar da sanarwar bullar cutar Kwalara a kasar tare da yin sanadiyyar mutuwar mutane da dama.

Rahotonni sun bayyana cewa wadanda suka kamu da cutar ya zuwa yanzu sun kai mutum 62 cikin mutane 83 da tun da fari aka yi zargin sun kamu da cutar a wani kauye, yayin da sha-biyu daga ciki suka rasa rayukan.

Gwamnan lardin da lamarin ya faru, Felix Nguele wanda ya bayyana haka a wata tattaunawa da manema labarai ya ce a yanzu haka an fara gudanar da allurar rigakafi a yankin da kwalarar ta bulla.

Nguele, ya kara da cewa wannan ne karon farko da ta bulla a watannin da suka gabata, inda ta hallaka mutane da dama ba tare da gano dalili ba, sai yanzu.

Sai dai hukumomin lafiya a kasar na zargin gurbatar muhalli a yankunan ne ya haifar da matsalar musamman a yankin Londji.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!