Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Bayan cikar wa’adi: Rashin sabunta lasisi zai hana direbobin adaidaita sahu hawa titi a Kano – KAROTA

Published

on

Hukumar KAROTA a jihar Kano ta ce, daga ƙarshen watan Maris na 2022 za ta haramtawa duk direban adaidaita sahun da bai sabunta lasisinsa ba hawa kan titi.

Mai baiwa gwmana shawara kan harkokin hukumar KAROTA Alhaji Nasir Usman Na’ibawa ne ya bayyana haka ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan Freedom Radio.

Shirin ya mayar da hankali kan matakin da hukumar zata dauka kan duk direban adaidaita sahun da bai sabunta lasisinsa ba.

“Tun a ƙarshen watan Fabrairu wa’adin da aka cimma tsakanin hukumar KAROTA da ƙungiyoyin direbobin adaida sahun ya cika, amma kuma mun ƙara musu wa’adi ne domin ganin halin da ake ciki a yanzu” a cewar Na’ibawa.

Ya ci gaba da cewa “Yanzu mun sanya wa’adin makonni uku ga direbobin na su sabunta lasisin su ko kuma mu hana su hawa kan titinan jihar Kano baki ɗaya”.

A watan Janairun 2022 ne matuƙa baburan adaidaita sahu a Kano suka shiga yajin aikin kwanaki uku kan batun sabunta lasisi, lamarin da ya gurgunta harkokin sufuri a jihar Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!