Connect with us

Labarai

Bello Turji ya saki fiye da mutane 100 da ya ke tsare da su

Published

on

Jagoran ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane a jihar Zamfara  Bello Turji, ya saki mutum sama da 100 da yake tsare da su a wani sabon yunkuri na samar da zaman lafiya da kawo karshen tashin hankali a jihar, da sakin  ya biyo bayan dogon tsarin tattaunawa da amincewa da shirin sulhu da ake gudanarwa a wasu yankunan Arewa maso Yamma. 

Shafin X, na Zagazola Makama kwararre kan harkokin tsaro  ya wallafa cewa wadanda aka sako sun hada da maza, mata da yara, kuma an mika su ga hukumomin yankin kafin kai su asibiti domin binciken lafiya da kulawa. 

Wata majiya da ta shiga cikin tattaunawar ta bayyana cewa an fara sakin mutane 36, sannan daga baya aka kara sakin wasu takwas, wanda ya kai jimillar 46 a matakin farko. 

Daga baya kuma aka ci gaba da sakin sauran, har adadin da aka sako ya kai sama da mutum 100 baki daya, da majiyar ta kara da cewa ana sa ran karin sakin mutane cikin kwanaki masu zuwa yayin da tattaunawa ke ci gaba. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!