Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Boss Mustapha ya bayyana tsaikon da aka samu na mika rahoton rikicin inshorar lafiya

Published

on

Babban sakataren gwamnatin taraya Boss Mustapha ya kare tsaikon da aka samu na mika rahoton kwamitin bincike kan  musababin rikici a hukumar dake kula da Inshorar lafiya ta kasa wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kafa.

Haka zalika shugaban kasar ya kafa kwamitin ne don bincikar zargin da ake wa babban sakatare a hukumar Inshrara lafiy ta kasa farfesa Usman Yusuf kan yin almundahar kudaden.

A yayin da yake karabar rahoton daga Kwamitin mutum 7, Boss Mustapha ya ce akwai bukatar gudanar da bincike mai zurfi a hukumar ta NHIS wanda ya sanya kwamitin ya kwashe makwanni 7 yana gudanar da bincike akai mai makwan makwanni 2 da gwamnatin tarayya ta bashi.

Haka zalika Boss Mustapha ya ce gwamnatin tarayya ta damu matuka kan rikicin hukumar ta NHIS,wanda ya sanya har ta kai ga dakatar da babban sakataren hukumar farfesa Usman Yusuf.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!