Labarai
Bouna Sarr ya amince ya wakilci kasar Senegal
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/09/WhatsApp-Image-2021-09-27-at-22.27.58.jpeg)
Dan wasan tawagar Bayern Munich , Bouna Sarr ya amince ya wakilci kasar Senegal a karo na farko bayan da a baya ya kaucewa haka.
Mai shekaru 29, Saar zai wakilci kasar ta Senegal a wasannin da zata fafata a watan Oktoba na 2021, na neman tikitin zuwa gasar cin Kofin Duniya na 2002 a kasar Qatar.
Dan wasan na da damar wakiltar kasashen Senegal da Guinea sai kasar Faransa , kasancewar bai taba wakiltar daya daga cikin kasashen ba a wasa na Babbar tawagar kasa.
You must be logged in to post a comment Login