Connect with us

Labarai

Buhari ya aike da sakon taya murna ga sabon shugaban kungiyar lauyoyi

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aike da sakon taya murna ga sabon shugaban kungiyar lauyoyi ta kasa Mr. Olumide Akpata wanda ya samu nasarar lashe zaben shugabancin kungiyar a baya bayan nan.

Hakan na cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Mr Femi Adesina.

Sanarwar ta bayyana sabo shugaban a matsayin wanda ya riki kungiyar tsahon shekaru biyu tare da fito da dabarun ciyar da ita gaba.

Kazalika sanarwar ta bukaci Mr Olumide da ya ci gaba da ayyukan tafiyar da kungiyar cikin tsari tare da sanya al’amuran gwamnati a kowanne matakai don samun shawarwarin da ya kamata don ciyar da kungiyar gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!