Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya ciyo bashin sama da naira tiriliyan ɗaya daga ƙasar China cikin shekaru 6 -DMO

Published

on

Wani rahoto daga ofishin kula da basuka na ƙasa DMO ya ce cikin shekaru 6 da suka gabata, gwamnatin shugaba Buhari ta ciyo bashin  dala biliyan biyu da miliyan biyu daga ƙasar China.

 

Rahoton ya bayyana cewa ƙididdigar basukan da ake bin Najeriya ya zuwa ƙarshen watan yunin shekarar 2015, ya tsaya ne akan dala biliyan ɗaya da miliyan talatin da takwas.

 

Yayin da ya zuwa ranar talatin da ɗaya ga watan Maris basukan da ƙasar China ke bin Najeriya ya kai dala biliyan uku da miliyan arba’in.

 

A cewar ofishin na DMO basukan da ake karɓa daga China yana da kuɗin ruwa na kaso biyu da ɗigo hamsin, kuma za a biya ne cikin wa’adin shekaru ashirin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!