Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya kara wa’adin wata daya don hada layukan tarho da lambar NIN

Published

on

Gwamnatin tarayya ta kara wa’adin wata guda don ci gaba da yin rajistar hada layin dan kasa (NIN) da kuma layukan wayar tarho.

A baya dai gwamnatin ta ware wa’adin shida ga wannan wata na Afrilu a matsayin ranar karshe da za a gama aikin hada layukan wayar da lambar dan kasa (NIN), to sai dai yanzu an kara wa’adin zuwa ranar shida ga watan gobe na Mayu.

Ministan sadarwa da bunkasa fasahar tattalin arziki, Dr Isa Ali Pantami ne ya bayyana haka ga manema labarai jiya a Abuja.

Ya ce tuni ma’aikatar ta aikewa shugaba Buhari da bukatar neman karin wa’adin kuma shugaban kasar ya amince da hakan.

A cewar sa ya zuwa yanzu, an samu ci gaba sosai wajen hada layukan na waya da lambar dan kasa, inda mutane akalla miliyan biyu da dubu dari shida suke hada layukansu da lambar dan kasa (NIN) a duk wata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!