Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

CBN ta bai wa kamfanonin rarraba wutar lantarki naira biliyan 33 don sayo mitar wuta – NERC

Published

on

Hukumar kula da al’amuran wutar lantarki ta kasa ta ce babban bankin kasa CBN ya bai wa kamfanonin rarraba wutar lantarki jimillar naira biliyan talatin da uku da miliyan dari hudu don sayo mitar wutar lantarki

A cewar hukumar ta NERC tun farko bankin na CBN ya yi alkwarin bai wa kamfanonin naira biliyan hamsin da tara da miliyan dari biyu wanda tuni ya saki sama da naira biliyan talatin da uku.

Shugaban hukumar Injiniya Sanusi Garba ne ya bayyana haka yayin zantawa da kwamitin kula da harkokin samar da wutar lantarki na majalisar dattijai jiya a Abuja.

Ya ce shirin wani bangare ne na kokarin gwamnati na samarwa gidaje miliyan daya mitar wutar lantarki tsakanin watan Oktobar shekarar da ta gabata da watan Afrilu wannan shekarar.

Ya ce tuni an sayo mita guda dubu dari hudu da uku kuma har an mika su ga kamfanonin samar da wutar lantarki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!