Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Cibiyar AHIP ta bayyana damuwa kan karuwar cin zarafin ‘dan-adam da ke karuwa a Kano

Published

on

Wata Cibiya mai rajin tallafawa rayuwar Iyali da dakile cin zarafin bil’adam ta AHIP, ta bayyana damuwarta kan karuwar cin zarafin ‘dan-adam da ke karuwa a Jihar Kano.

Babban jami’in tsare-tsare na cibiyar Malam Abba Bello Ahmad ne ya bayyana hakan, ta cikin shirin Mu Leka Mu Gano na musamman na nan tashar Freedom Rediyo.

Malam Abba Bello Ahmad, ya bayyana cewa, adadin cin zarafin da ke karuwa a Jihar nan ya hadar da na sabani a tsakanin Iyali, tare da cin zarafin kananan yara musamman ma ‘ya’ya mata, wanda hakan ke neman zama ruwan dare a halin yanzu.

Haka zalika ya kara da cewa, kunya da boye laifin masu aikata cin zarafin yaran da aka yi wa fyade na daga cikin dalilan da ke janyo karuwar aikata laifukan, sakamakon kin tona asirin wadanda aka kama.

Ya kuma ce, rashin koyar da yara wasu daga cikin hanyoyin da za su kare kansu daga fadawa hannun bata-gari da iyaye ke yi, na taka rawa wajen kara haifarwa yaran matsala.

Malam Abba Bello Ahmad ya bayyana cewa, samar da hukunci mai tsanani kan wadanda aka kama da laifin cin zarafin yara musamman ma fyade, hakan zai taimaka matuka wajen dakile yaduwar aikata laifin fyaden.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!