Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mata ‘yan kasa da shekaru 9 aka fi yiwa Fyade a Najeriya

Published

on

Cibiyar kula da wadanda suka gamu da Ibtila’in fyade da cin zarafi ta Asibitin kwararru na Murtala Muhammad tace yara mata yan kasa da shekaru 9 ne suka fi fadawa cikin ibtila’in fyade da kuma cin zarafin su a nan Kano.

Sakataren cibiyar kula da wadanda suka gamu da matsalar fyade da cin zarafi mai taken “Waraka” Malam Abba Bello ne ya bayyana hakan ta cikin shirin Muleka Mugano na nan Freedom Radio wanda ya mayar da hankali kan yadda aikata laifin fyade ke kara ta’azzara a wannan lokaci.

Malam Abba yace cibiyar tana samun bayanai ne daga wajen hukumomin gwamnati daban-daban kan laifukan fyade da cin zarafin mata masu karancin shekaru, don haka akwai bukatar al’umma su tashi tsaye wajen ganin an kawo karshen aikata fyade.

Sakataren Cibiyar Abba Bello yace babban abin takaicin shine yadda mutane ke nunawa wadanda suka gamu da ibitila’in fyade kyara ga tsangwama ba tare da la’akari da irin mayuyacin halin da suka tsinci kansu a ciki ba, wanda hakan ke jefa rayuwar su cikin mummunan yanayin da ya fi na fyaden.

Malam Abba Bello yayi kira ga iyaye mata da maza musamman manyan mata da suka taba gamuwa da matsalar fyade dasu rika kai rahoto ga Hukumomin tsaro kasancewar shiru da baki da ‘iyaye mata keyi na kara ta’azzara matsalar ta fyade.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!