Connect with us

Kiwon Lafiya

Citad ta wayar da kan matasa kan yadda za su sami cigaba a rayuwar su

Published

on

Tsohon shugaban hukumar kula da ‘yancin dan Adam ta kasa Farfesa Muhammad Tabi’u ya shawarci matasa dasu maida hankali wajen rungumar tsarin da zai kaisu ga cimma manufofin sun a ci gaban rayuwa.

Farfesa Muhammad Tabu’u na sashen shari’ar musulunci dake jami’ar Bayero anan Kano ya bayyana hakan ne yayin taron dake nusar da matasa harkokin shugabanci da cibiyar bunkasa fasahar sadarwa da ci gaban al’umma ta CITAD ke shiryawa wata-wata.

Ya ce ya zama wajibi matasa su dauki ta’adar shugabanni nagari don fuskantar matsalolin da suka dabai-baye tattalin arziki da ci gaban kasa baki daya.

daraktan cibiyar bunkasa fasahar sadarwa da ci gaban al’umma ta CITAD Yunusa Zakari Ya’u ya ce manufar shirin shine don fadakar da matasa yadda za su fuskanci kalubalen rayuwa tare da yin nasara kan abubuwan da suka saka a gaba.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!