Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Coronavirus ta bulla a Sokoto

Published

on

Cibiyar dakile cutuka masu yaduwa ta kasa NCDC ta ce an samu bullar cutar Covid-19 a jihar Sokoto.

Cikin sanarwar da hukumar ta wallafa a shafinta na Twitter ta ce an samu mutum guda dake dauke da kwayar cutar Covid-19 a jihar Sokoto.
Wakilin mu dake Sokoto Umar Ahmad Baffa ya shaida mana cewa tuni gwamnan jihar ta Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya bada sanarwar samun mai dauke da cutar a jihar.

A sanarwar NCDC ta ce a yau Litinin an samu karin mutane 38 da suka kamu da cutar a sassan Najeriya.

Kididdigar NCDC ta daren Litinin dinnan ta ce yanzu haka Najeriya tana da mutane 665 da suka kamu da cutar, inda 188 daga ciki suka warke sarai, guda 22 kuma suka mutu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!