Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Karin mutum 23 sun kamu da Coronavirus a Kano

Published

on

Cibiyar dakile cutuka masu yaduwa ta kasa NCDC ta ce mutane 23 ne suka kamu da cutar Coronavirus a Kano ranar Litinin.

Sanarwar da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce yanzu Kano tana da mutane 59 da suka kamu da cutar an samu karin mutane 38 da suka kamu da cutar ranar Litinin a sassa daban-daban Najeriya.

Jihar Kano ce kan gaba a yau Litinin da ta samu karin mutane 23 sai jihar Gombe da ta samu mutane 5, jihar Kaduna ta samu karin mutum 3 sai jihar Borno da ta samu karin mutum 2, ita ma jihar Abia ta samu mutane 2 birnin tarayya Abuja ta samu karin mutum 1 Sokoto ta samu mutum 1 sai jihar Ekiti ita ma an samu karin mutum 1.

Har ila yau hukumar ta NCDC ta ce a ranar Litinin din adadin wadanda suka kamu da cutar a Najeriya ya kama 665 inda mutum 188 suka warke, mutane 22 kuma suka mutu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!