Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid-19: An baiwa gwamnatin Jigawa tallafin kayan abinci kan Corona

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa tace ta karbi tallafin kayan abinci tirela 93 daga gamayyar kungiyar ‘yan kasuwa ta kasa, domin rabawa talakawa mabukata yayin dokar zaman gida ta sanadin corona.

Kwaminshinan lafiya kuma Shugaban kwamatin karta kwana a jihar Jigawa Dakta Abba Umar ne ya shaidawa wannan shiri haka da yammacin litinin din nan.

Kwaminshinan yace tuni suka fara aikin tan-tance wadanda ke sahun gaba ta fuskar bukata daga kananan hukumomin jihar, wanda a karon farko za’a fara bada tallafin da masu bukata ta musamman, kafin daga bisa ni a buda abin zuwa duk wani mai bukata.

Dakta Abba yace dama dai tuni sukayi rabon masara ga al’umma da kuma shinkafa da gero ga almajirai, a kananan hukumomin da dokar kulle ta shafa.

Labarai masu alaka:

Mutane 55 sun warke daga Corona a Jigawa

Yadda dokar kulle ke gudana a Jigawa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!