Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid-19: An janye dokar kulle a Ringim

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta sanar da dage dokar kulle a karamar hukumar Ringim ta jahar jigawa sakamakon nasarar da ake samu wajen yaki da cutar a jihar.
Shugaban kwamatin karta-kwana na dakile yaduwar cutar Covid-19 a jihar Jigawa Dakta Abba Umar ne ya bayyana haka da yammacin Alhamis din nan.
Dakta Abba yace an dage dokar ne a garin Ringim da kuma sabon Garin Yaya ta karamar hukumar Taura samakon rashin yaduwar cutar zuwa ga wasu tun bayan mutane na farko a garuruwan da aka samu na dauke da cutar ta corona Virus.
Haka kuma Dakta Abba ya kara da cewa, akwai wasu gwaje-gwajen mutane da ake jiran fitowar su, kuma shi ne zai haska makomar garuruwan Gwaram da Birnin Kudu na yiwuwar a dage musu dokar kokuma aci gaba da zaman gida.

Labarai masu alaka:

An gano karin mutane 14 dauke da cutar Covid-19 a Jigawa

Covid-19: Cibiyar gwajin Corona zata fara aiki a Jigawa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!