Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Covid-19: Buhari ya hana jami’an gwammati fita kasashen waje

Published

on

Shugaban kasa Muhamamdu Buhari ya dakatar da ma’aikatan gwamnatin kasar nan daga fita kasashen waje sakamakon bullar cutar Coronavirus.

Sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala wani zama na musamman da majalisar zartarwa ta kasa tayi kan cutar ta Coronavirus, kamar yadda mai taimakawa shugaban kasa akan kafafan sadarwa na zamani Bashir Ahmad ya wallafa a shafin sa na Twitter.

Bashir Ahmad ya ce shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da kafa wani kwamiti na musamman wanda ya kunshi mutane goma sha uku, da zaiyi aiki kan magance cutar ta Coronavirus wanda Boss Mustapha zai shugaban ta.

Sai kuma tsohon shugaban hukumar yaki da cuta mai karya garkuwar jiki ta kasa Dr. Sani Aliyu a matsayin babban jami’in kwamitin.

*BS.*

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!