Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

KannyWood

Naziru ya yi Murabus daga Sarkin Wakar Sarkin Kano

Published

on

Fitaccen mawakin Hausar nan, Nazir M. Ahmad, yayi murabus daga sarautar sa ta Sarkin Wakar Sarkin Kano.

Cikin wata sanarwa da Nazirun ya sanyawa hannu mai dauke da kwanan watan ranar 13, ga watan Maris din da muke ciki, Naziru ya ce ya ajiye sarautar nan take.
Sannan yayi godiya ga masarautar Kano bisa bashi wannan sarauta da ya shafe shekara guda akan ta.

Idan zaku iya tunawa dai a watan Disamba na shekarar 2018 ne, Sarkin Kano na wancan lokacin Muhammadu Sanusi II ya nada Nazir M. Ahmad matsayin Sarkin Wakar Sarkin Kano.

Naziru M. Ahmd yayi suna wajen wakar sarakuna.

Wakar sa mai farin jini da ya yiwa Sarkin Kanon na wancan lokaci ita ce “Mata ku dau turame” wadda har yanzu jama’a ke cigaba da yayin ta, ta yadda akan sanya wakar a mafi yawan bukukuwa da ake gudanarwa a kasar Hausa, kamar yadda wani rahoton BBC Hausa ya bayyana a makon da ya gabata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!