Labaran Wasanni
COVID-19: Senegal na shirin ficewa daga wasan karshe na share fagen shiga gasar Olympic
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/06/amm.jpeg)
Kasar Senegal za ta fice ba tare da shiri ba daga wasannin kwallon kwando na share fagen shiga gasar Olympic sakamakon barkewar cutar Corona a kasar.
Hukumar kwallon Kwando ta duniya FIBA ce ta tabbatar da tilastawa kasar ficewa daga wasannin duba da yadda annobar Corona take kara kamari a kasar.
Rahotanni na cewa, ‘yan wasa uku da kuma wani mamba a tawagar ‘yan wasan kasar ta Senegal sun kamu da cutar COVID-19.
Haka ne ya tabbatar da cewa kasar ba za ta samu damar zuwa kasar Serbia ba domin fafata wasannin karshe da za a fara ranar Laraba 30 ga watan Yunin 2021.
You must be logged in to post a comment Login