Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Cunkuson mutane a cibiyoyin samar da katin dan kasa a Kano bakon al’amari ne – NIMC

Published

on

Hukumar samar da lambar katin dan kasa a nan Kano ta ce, cunkoson al’umma da ake samu a cibiyoyin samar da katin dan kasa a jihar Kano a kwanakin nan, bakon lamari ne da ba a taba ganin irinsa ba tun bayan da aka samar da hukumar.

Daraktan kula da hukumar shiyyar Kano Alhaji Lawal Yahaya ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala shirin “Barka da Hantsi “na nan tashar Freedom Radio da shirin ya mayar da hankali kan yadda ake samun cunkoson mutane a wajan yin rajistar a kwanakin nan.

Ya ce, cunkoson na da alaka da yadda gwamnatin tarayya tayi barazanar kulle layukan wayar da basu hade layin nasu da lambar katin dan kasa ba, wanda hakan ya sanya jama’a suka bazama domin mallakar katin a yanzu.

Alhaji Lawan Yahaya ya ce, cunkoson jama’ar na barazana ga lafiyarsu baya ga rashin wadatattun kayan aiki a hukumar wanda ke kara ta’azzara cunkoson.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!