Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

INEC ta samar da sabon tsarin yin rajistar katin zabe ta Internet

Published

on

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC, ta ce za a yi aikin rajistar samar da katin zabe ta Internet a wasu cibiyoyin samar da katin, a kokarin magance matsalolin cinkoson masu jefa kuri’a a cibiyoyi daban-daban a Najeriya.

A cewar hukumar ta INEC sabon shirin zai yi tasiri wajen rage cunkoson a cibiyoyin yin rajistar.

Kwamishinan yada labarai da ilimantar da masu jefa kuri’a na hukumar, Festus Okoye ne ya bayyana hakan yayin zantawarsa da jaridar Punch a jiya Litinin 22 ga watan Maris din 2021.

Yace, sabon tsarin zai bada damar yin rijistar ta Internet ba sai mutum yaje cibiyoyin ba wannan hakan zai zo ne gabanin zaben shekarar 2023.

Idan za a iya tunawa dai hukumar INEC tun a watan Nuwamba na shekarar 2020 ta yi alkawarin cewa za ta ci gaba da rijistar masu kada kuri’a, wanda aka dakatar tun a watan Agustan 2018, inda tayi alkawarin ci gaba da yi a zangon farko na shekarar 2021.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!