Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Da ɗumi-ɗumi: Kotu ta yanke wa Sadiya Haruna ɗaurin watanni shida

Published

on

Kotun Majisitiri da ke filin jirgin saman Kano ta yanke hukunci ɗaurin watanni shida ba tare da zaɓin tara ba.

Yayin zaman kotun na yau Mai Shari’a Muntari Garba Ɗandago ya yanke mata wanann hukuncin ne bisa kalaman ɓatanci da ta yi ga wani mai suna Isah I. Isah a shafinta na Instagram.

Idan zaku iya tunawa dai a shekarar 2019 aka samu saɓani tsakanin Sadiyan da Isah.

Daga nan ne kuma ta yi masa kakkausan kalamai a cikin wasu faya-fayan bidiyo da ta riƙa wallafawa.

Wannan dai na zuwa ne mako guda bayan da Sadiyan ta sanar da cewa wasu na ƙoƙarin yin garkuwa da ita.

Sadiya Haruna ta yi fice a kafafen sada zumunta wajen yawan cece-kuce.

Ko a shekarar da ta gabata wata kotun ta yanke mata hukuncin komawa makarantar Islamiyya bayan da Hisbah ta zarge ta da bayyana tsiraici da sakin baki a kafafen sada zumunta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!