Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Kotu ta yanke wa Sadiya Haruna hukuncin komawa Islamiyya

Published

on

Yau Litinin rundunar ƴan sandan jihar Kano ta gurfanar da wata mai amfani da kafafen sada zumunta Sadiya Haruna a gaban kotu.

An gurfanar da ita a kotun shari’ar Musulunci da ke hukumar Hisbah, bisa zargin yaɗa batsa a kafafen sada zumunta.

Yayin zaman kotun mai shari’a Ali Jibrin Ɗanzaki ya yanke mata hukuncin sanyata a makarantar Islamiyya ta Darul Hadith har tsawon wata shida.

Za ta riƙa zuwa kullum tare da rakiya jami’in hukuma.

Sannan za ta riƙa sanya hannu a duk sanda ta je.

Sadiya Haruna dai ta shahara a kafafen sada zumunta wajen yaɗa hotuna tare da kalaman batsa.

Tun da farko rundunar ƴan sandan jihar Kano ce, ta karɓi ƙorafi daga mutane kan ayyukan matashiyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!