Connect with us

Labarai

Da dumi dumi: Gwamna Alia na Benue ya rushe Majalisar zartaswar jihar

Published

on

Gwamna Alia na Jihar Benue ya rusa Majalisar Zartaswar Jihar tare da umurtar kwamishinoni da su mika ragamar mulki ga sakatarorin dindindin na ma’aikatunsu.

 

Cikin wani bayani da mai magana da yawun gwamnan, Tersoo Kula ya fitar, ya nuna cewa gwamnan ne da kansa ya sanar da wannan mataki a ƙarshen taron majalisar zartarwa ta jihar Benue na karo na 12 a shekarar 2025.

 

Gwamna ya nuna godiyarsa ga dukkan tsofaffin kwamishinonin da suka yi aiki tare da shi na tsawon shekaru biyu, yana mai kiraye-kiraye ga wadanda ba za a sake naɗa su ba ko kuma ba za a kira su ba, da su ci gaba da kasancewa cikin jam’iyya da haɗin gwiwa da tsarin, domin dai kawai suna ba wasu ‘yan kasa damar su ma su samu zarafin bada gudunmawarsu.

 

Ya ƙara da cewa, rushewar bata shafi Shugaban Ma’aikata na jihar ba ta shafi kwamishinoni ne kawai.

 

Da yake magana a madadin sauran kwamishinonin da aka rushe, Barista Bemsen Mnyim, ya godewa gwamna saboda damar da ya ba su na yin hidima ga jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!