Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamna Samuel Ortom ya je gaban kwamitin majalisar dattijai kan binciken kashe-kashen jihar sa

Published

on

Gwamnan jihar Benue Samuel Ortom, ya ziyarci kwamitin majalisar dattijai kan binciken kashe-kashen da ke faruwa a jihar Benue.

A makon da ya gabata ne Kwamitin majalisar Dattawa kan kashe-kashen da ke faruwa a jihar ta Benue, ya gabatar da rahoton sa, inda ya ce babban Sufeton yan sandan kasar nan ya gaza yin abinda ya da ce kan rikicin da ya taso a jihar ta Benue wajen kama wa tare da gurfanar da wadanda ke da hannu cikin rikicin.

Cikin rahoton kuma kwamitin ya bayyana cewa babban Sufeton yan sandan kasar nan ya ce rundunar ta samu nasarar chafke mutane 145 da ke da hannu cikin al’amarin.

Daga nan ne kuma majalisar ta yi watsi da rahoton kwamitin sakamakon rashin jiyo ta bakin gwamnan jihar kan matsalolin tsaro da ke faruwa a jihar, tare da umartar kwamitin da ya koma don jin ta bakin gwamnan kan batun.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!