Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar Dattawa ta dakatar da Tinubu daga tura sojoji kasar Nijar

Published

on

Yan majalisar dattawan Nijeriya sun yi watsi da bukatar shugaba Bola Ahmed Tinubu na neman izinin tura dakarun kasar zuwa Jamhuriyar Nijar bayan kungiyar ECOWAS ta ce, za ta yi amfani da karfi domin maido da zababben shugaban kasar da aka yi wa juyin mulki.

 

‘Yan majalisar sun sanar da matsayarsu ne a wani zama da suka gudanar a a jiya Asabar.

 

‘Yan Majalisar sun Kuma jinjinawa shugabannin Kungiyar Bunkasa tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS kan jajircewarsu wajen ganin sun maido da kasar kan tsarin dimokradiyya.

 

Sai dai sanatocin ba su amince da bukatar daukar matakin soji a kasar ba, saboda alakar da ke tsakanin kasashen biyu.

 

A maimakon haka, sanatocin sun bukaci shugaba Tinubu da ya kara kaimi ta fuskar zaman sulhu tare da sojojin da suka hambarar da mulkin shugaba Mohamed Bazoum.

 

 

 

 

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!