Connect with us

Labarai

Dakile satar amsa ne ya janyo faduwar dalibai a JAMB- Ministan Ilimi

Published

on

Ministan ilimin na Najeriya Dakta Tunji Alausa, ya bayyana cewa, hana satar amsa ne ya janyo faduwar dalibai a jarawabar shiga manyan makarantun gaba da sakandire ta JAMB a bana.

Tunji Alausa, ya bayyana hakan ne yayin tattaunawa da gidan talabijin na Channels a Talatar makon nan.

Haka kuma ya ce, hakan ya nuna yadda tsarin rubuta jarabawar ya dakile satar amsa da dalibai ke yi a baya.

A ranar Litinin din makon nan ne hukumar shirya jarrabawar shiga makarantun gaba da Sakandare JAMB ta fitar da sanawar cewa cikin dalibai miliyan 1 da dubu dari tara da hamsin da suka rubuta jarabawa, kimanin miliyan 1, da dubu 534 da dari 654 ne suka samu maki kasa da 200.

Haka kuma, hukumar ta ce, dalibai dubu 12 da dari 414 ne suka samu maki 300 zuwa sama.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!