Labarai
Daliban da gwamnatin Abba ta tura India karatun Digiri na 2 sun nemi daukin mahukunta

Daliban da gwamnatin Kano ta tura kasar Indiya domin karatun digiri na biyu, sun bukaci daukin mahukunta, bayan karewar takardun izinin zamansu a kasar.
Daya daga cikin daliban, Sa’id Idris Usaini, ya ce, sun kai korafe-korafe daban-daban ga mahukunta, amma har yanzu ba a shawo kan matsalar ba.
Sa’id Idris Usaini, ya kara da cewa ci gaba da zamansu a haka zai iya jefa rayuwarsu cikin damuwa, don haka ne su ke neman a agaza musu domin ci gaba da gudanar da rayuwarsu bisa tanadin doka.
You must be logged in to post a comment Login