Labarai
NLC ta bukaci gwamnatin tarayya ta samar da hanyoyin saukaka hauhawar kayayyaki

Kungiyar Kwadago ta Najeriya , NLC, ta bukaci gwamnatin tarayya da ta gaggauta bijiro da hanyoyin da za su samar wa da yan mutane sauki da kuma karin albashi na musamman ga ma’aikata yayin da farashin man fetur ke kara tashi.
Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya ce karin farashin man fetur zai kara tsadar sufuri da abinci da sauran bukatun yau da kullum.
NLC ta kuma bukaci gwamnati ta tabbatar da sayar da danyen mai ga matatun cikin gida da Naira, domin rage tasirin matsalar farashin mai ga ‘yan Najeriya.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa wasu daga cikin yan kasar nan sun fara tafiya da kafa mai nisa, sakamakon tashin farashin man fetur, domin ragewa kansu kudin sufuri.
You must be logged in to post a comment Login