Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Dan majalisar mai wakilya mazabar Pengana a jihar Filato ya mutu

Published

on

Dan majalisar dokoki mai wakiltar mazabar Pengana a jihar Filato daga jam’iyyar APC mai mulki Ezekiel Afon ya mutu.

Sakataren jam’iyyar APC na jihar ta Filato Bashir Sati ya tabbatar da rasuwar marigayin Ezekiel Afon a tattaunawar sa da manema labarai a Jos babban birnin jihar ta Filato.

A cewar rahoton Mr Afon shi ne ya sake lashe zaben majalisar dokoki jim kadan bayan sanar da cewa shi ne ya lashe zaben mazabar sa, kasancewar yana fama da rashin lafiyar aka dauke shi zuwa a wani asibiti dake kasashen waje, amma kuma jim kadan da sanar da cewa ya lashe zaben aka bayyana cewar ya rasu a jiya Lahadi.

Sakataren jam’iyyar APC ya ce ya kado matuka da rasuwar marigayin, bayan da jam’iyyar APC ke tsaka da gudanar da murnar sake lashe zaben sa. An dai zabe Mr Ezekiel Afon a shekara ta 2015 a karkashin jam’iyyar PDP, sai dai daga baya ya sauya sheka zuwa jam’iyya mai ci ta APC yayin da aka sake zabar a ranar Asabar a mazabar ta Pengana

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!