Connect with us

Labarai

Dan tsami ya janyo mana rashin ciniki – Masu sana’ar sayar da lamurje a Kano

Published

on

Masu sana’ar sayar da lemeon lamurje sun yi korafin cewa suna fama da rashin ciniki wanda suka alakanta hakan da batun dan tsami da hukumomi suka ce ya yi sanadiyar wasu mutane sun rasa rayukansu a Kano a kwanakin baya.

A cewar mutanen tun bayan da aka yi zargin cewa sinadarin dan tsami ne ya janyo wasu mutane suka mutu sannan wasu da dama suke karbar magani a asibiti, suka fara ganin koma baya a cinikinsu.

Malam Awwalu Nagarta flavor daya ne daga cikin masu sana’ar sayar da kayan hadin lemon a kasuwar Rimi da ke Kano, shima cewa ya yi, ko da su da suke sayar da kayan hadin lemon sun shiga mawuyacin hali sanadiyar rashin ciniki da suke fama da shi a wannan lokaci.

‘‘Sanin kowane babu lokacin da sana’ar mu ta fi garawa kamar lokacin azumi amma a bana lamarin ya canja’’ a cewar sa.

Ya kuma godewa gwamnati sakamakon yadda ya ce ta shigo don tsaface sana’ar tasu ta hanyar fitar da baragurbi da ke gurbata sana’ar ta su da kayayyaki marasa inganci.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!