Connect with us

Labarai

Direbobin motocin dakon Fetur da Gas na shirin tsunduma yajin aiki

Published

on

Ƙungiyar ma’aikatan dakon Man Fetur da  Iskar Gas ta  NUPENG, ta tabbatar da cewa za ta fara yajin aikin da ta sanar, daga yau Litinin, 8 ga Satumba.

 

Shugaban kungiyar ta NUPENG, Williams Akporeha, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

 

Ta cikin sanarwar, ƙungiyar ta bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta tuntubi NUPENG domin hana yajin aikin, amma hakan ba zai hana aiwatar da yajin ba, har sai bayan ganawar da za a yi da gwamnati a yau.

 

A cewarsa matakin ya samo asali ne daga shirin kamfanin Mai na Dangote na shigo da sabbin manyan motoci masu amfani da makamashin CNG guda 4,000 da za su rika kai mai kai tsaye zuwa gidajen Mai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!