Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dokar CBN bata shafi hada-hadar ko musayar kudi ta yanar gizo ba- Dr Abdussalam Kani

Published

on

Wani Masanin tattalin arziki dake kwalejin Sa’adatu Rimi a nan Kano, Dr Abdussalam Muhammad Kani ya ce, dokar takaita cirar tsabar kudi a bankuna bashida alaka da ajiya ko musayar kudin a asusun banki ta yana gizo.
Dakta Abdussalam Muhammad Kani ya bayyana hakan ne yayin tattaunawarsa da Freedom Radio.

Wanda ya ce sabuwar dokar bankuna tsarine da zai taimaka ta hanyar kawarda barazanar rike manyan kudade a hannu mutane, ko ajiye su gidajen su.

Yana mai cewa dokar za kuma ta rage yawaitar kudaden jabu da suke yawo, dakuma koyardar halayyar ajiye kudi a bankuna tareda gudanar da hada-hadar kudaden cikin sauki ta hanyar aikewa dasu ta yana gizo.

Sai dai Dakta Kani yace, karancin bankuna a kasar nan zai iya haddasa hau-hawar farashi dama cinikin naira kamar cinikin dala sanadiyar wannan doka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!