Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

 Dokar kare haƙƙin yara ta tsallake karatu na biyu

Published

on

Dokar kare haƙƙin yara, ta tsallake karatu na biyu a zauren majalisar dokokin jihar Kano.

Dokar ta kai wannan mataki ne a zaman majalisar na Litinin din nan bayan da aka yi mata karatu na farko a ranar Talata.

Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ne dai ya aike wa majalisar takardar neman yin nazari kan ƙudurin tare da sahalewa dokar.

Da yake karanto wasu daga cikin sassan da dokar ta ƙunsa, shugaban masu rinjaye na majalisar Alhaji Labaran Abdul Madari, ya ce, dokar ta yi tanadin kare yara daga cin zarafi da wasu sauran batutuwa.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!