Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rashin tsaro da lalacewar hanya ne ke haddasa wahalar mai a Nigeriya-IPMAN

Published

on

Kungiyar IPMAN ta alakanta rashin kyan hanya, da kuma karancin tsaro a matsayin abinda yake haddasa wahalar man da ake fama dashi a Arewacin kasar nan.

shugaban kungiyar dillalan man fetur ta kasa reshen Jihar Kano IPMAN Alhaji Bashir dan Malam ne ya bayyana hakan yayin tattaunawarsa da Freedom Radio.

Bashir Dan Malam ya ce da hanyar da motocin da suke dauko man daga Kudu zuwa Arewa basu lalace ba, motocin dakon man baza su rinka shan wahala kafin kawo man ba.

Wanda yace rashin cikakken tsaro ma akan hanyar na taka rawa wajen hana motocin nasu zirga-zirga da daddare.

Yana mai cewa wannan matsalar suma tana damunsu, don haka kungiyar ke kira da DSS din dasu sanya baki wajen gyara hanyar, da samar da tsaro. tare kuma da bawa ‘yan kasuwa dala, don shawo kan wannan matsalar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!