Connect with us

Labarai

DSS ta saki Fulani 3 da ta kama bisa zarginsu da ta’addanci

Published

on

Humumar tsaron farin kaya ta DSS ta saki wasu mutane uku Fulani da ta kama yayin da suke sauka daga jirgi bayan sun dawo daga aikin Hajji a watan yunin 2024

DSS ta bayyana hakan ne a wani taron manema labarai a shalkwatar ta da ke Abuja inda ta ce, ta kama mutanen ne bisa zargin su da hannun a ayyyukan yin garkuwa da mutane a yankin arewacin Najriya.

Wadanda hukumar ta kama sun hadar da Rabi’u Alhaji Bello da Umar Ibrahim da Bammo Jajo Sarki, wadanda dukan su yan jihar Kwara ne. 

Hukumar ta DSS ta ce, ta kammala bincike a kan su kuma ba ta same su da laifin komai ba, don haka ta bai wa kowannen su kyautar naira miliyan daya.

Kungiyoyin Fulani dai sun sha kokawa kan kama mutanensu game da zargin garkuwa da mutane da kuma ta’adanci ba tare da wata hujja ba inda suka ce hakan abin takaici ne.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!