Connect with us

Labarai

ECOWAS ta amince da John Mahama a matsayin ɗan takarar Shugaban Kungiyar Tarayyar Afrika (AU)

Published

on

Majalisar Ministocin kungiyar raya tattalin arzikin kasashen Afrika ta yamma ECOWAS ta amince da Shugaban Ghana, John Mahama, a matsayin ɗan takarar kungiyar da zai nemi kujerar Shugaban Kungiyar Tarayyar Afrika (AU) a shekarar 2027, lokacin da jagorancin zai koma yankin Yammacin Afrika.

An cimma wannan matsaya ne a taron ministocin karo na 95 da aka gudanar a babban birnin tarayyar Najeria Abuja, inda aka bayyana Ghana a matsayin muhimmiyar ƙasa a ECOWAS wadda ke ba da gudunmuwa ga martabar ƙungiyar a matakin duniya.

Jaridar Premium Times ta ambato Ministan Harkokin Wajen Ghana, Sam Ablakwa, ya bayyana cewa shugabannin kasashen ECOWAS za su tabbatar da wannan matsaya a gobe Lahadi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!