Connect with us

Labarai

ECOWAS ta bayyana damuwa kan harin soji da gwamnatin shugaba Trump ta kai Venezuela

Published

on

Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afrika  ECOWAS ta bayyana  damuwa kan harin sojin Amurka da gwamnatin Shugaba Donald Trump ta kai a Venezuela.

A wata sanarwa da ta fitar a Abuja, ECOWAS ta amince da haƙƙin kowace ƙasa na yaƙi da manyan laifukan ƙasa da ƙasa kamar ta’addanci da safarar miyagun ƙwayoyi, amma ta jaddada cewa dole ne a aiwatar da hakan bisa ƙa’idojin dokar ƙasashen duniya da kuma mutunta ikon ƙasashe masu cin gashin kansu.

Kungiyar ta tunatar da al’ummar duniya wajibcin mutunta cikakken ikon ƙasa da yancinta, kamar yadda Sashe na 2(4) na Kundin Tsarin Majalisar Ɗinkin Duniya ya tanada, wanda ke hana amfani da ƙarfi ko barazanar amfani da ƙarfi kan wata ƙasa.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!