Connect with us

Labarai

EFCC za ta kama masu yi mata sojan gona a social media

Published

on

Hukumar da ke hana cin hanci da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati ta EFCC ta ce za ta fara kama mutanen da ke amfani da sunanta ko tambarinta a wasannin kwaikwayo ba tare da izini ba.

Hakan na kunshe cikin wani sakon bidiyo da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook da safiyar Asabar, dauke da alamar gargadi ga jama’a a rubuce.

A cikin sanarwar, hukumar ta nuna takaici kan yadda ake amfani da sunanta, tambarinta ko kakin jami’anta a wasannin barkwanci da bidiyoyin sada zumunta domin neman suna ko mabiya, inda ta ce hakan laifi ne kuma bata suna ne.

EFCC ta kara da cewa ta lura da yadda ake amfani da sunanta ko tambarinta a irin wadannan shirye-shirye ba tare da izini ba, lamarin da ya sabawa doka.

A karshe, hukumar ta gargadi jama’a da su guji hakan, tana mai cewa za ta fara kama duk wanda aka samu da aikata irin wadannan laifuka tare da gurfanar da shi a gaban kotu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!