Labarai
Sojoji sun kuɓutar da mutanen da aka yi garkuwa da su a Filato

Sojojin Najeriya sun ceto mutane da dama da aka yi garkuwa da su tare da lalata wasu sansanonin ’yan bindiga yayin wani samame da suka kai dajin Daji Madam da ke tsakanin Ƙananan Hukumomin Wase da Kanam a Jihar Filato.
Majiyoyin soji sun ce farmakin ya mayar da hankali ne kan sanannun maɓoyar ’yan bindiga da suka haɗa da Dogo Ruwa da Bogwas.
An ƙaddamar da wannan farmaki ne bayan yawaitar hare-hare, sace-sacen da kashe-kashe ga mutane a Wase da Kanam, inda mazauna yankin da jami’an tsaro da ’yan banga da dama suka rasa rayukansu.
Ɗaya daga cikin waɗanda aka sace, Waziri Usman, ya ce ya shafe kwanaki 13 a hannun masu garkuwa da mutane bayan an sace shi tare da wasu yayin da suke dawowa daga aikin gawayi.
A cewar sa sun kai su cikin daji a kan babura, inda suka yimusu duka sannan suka hana su abinci, kuma suka basu gurbataccen ruwa.sai kuma suka nemi kuɗin fansa har Naira miliyan 30, in ji shi.
Ya ce sun samu damar tserewa ne lokacin da sojoji suka tsananta kai farmaki tare da jiragen yaƙi suna shawagi a sama, lamarin da ya tilasta wa ’yan bindigar tserewa.
You must be logged in to post a comment Login