Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Enyimba ta dauki Finidi George a matsayin sabon mai horarwar ta

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Enyimba ta nada tsohon Dan wasan Najeriya Finidi George a matsayin sabon mai horas da ‘yan wasan ta.

Finidi George ya sakawa kungiyar kwantaragin shekaru 2 ne bayan da ya karbi mai horar da kungiyar ta Enyimba da kwantaragin shi ya kare a watan Augustan shekarar 2021 Fatai
Osho.

Ahmad Musa zai iya yiwa Najeriya wasanni 140-Vincent Enyeama

George ya buga wasa a kungiyar Ajax dake kasar Holland inda ya daukar mata kofin zakaru na Turai wato Champion league a shekarar 1995 sannan ya yi wasa a kungiyar Real Betis da Mallorca dake kasar Spain.

George, ya bugawa kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagles wasanni 62.

Ya kuma daukarwa Najeriya kofin Afrika a shekarar 1994 sannan ya wakilci kasar nan a gasar cin kofin Duniya a shekarar 1994 da 1998.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!