Connect with us

Ƙetare

Eritrea ta fice daga kungiyar kasashen Gabashin Afirka IGAD

Published

on

Kasar Eritrea ta sanar da ficewarta daga kungiyar kasashen Gabashin Afirka ta IGAD, tana mai zargin kungiyar da fatali da ka’idojin da aka kafa ta a kai da kuma gaza taka rawar gani wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

A cewar ma’aikatar harkokin wajen Eritrea, wadda ta fitar da bayanin ta cikin wata sanarwa ta ce kasar bata karuwa da kasancewarta karkashin kungiyar, musamman a bangaren samun aminci da zaman lafiya.

Wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da musayar kalamai masu zafi tsakanin Eritrea da makwabciyarta Habasha, lamarin da ke kara tayar da hankula a yankin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!